Home Back

"Lamarin Ya Yi Muni" Ƴan Bindiga Sun Kewaye Gari Guda, Sun Tafka Mummunar Ɓarna a Kaduna

legit.ng 2024/5/18
  • Rahotanni daga Kaduna sun nuna cewa ƴan bindiga sun kai kazamin hari kauyen Angwar Danko da ke ƙaramar hukumar Birnin Gwari
  • Wakilin yankin a majalisar dokokin jihar, Yahaya Ɗan Salio, ya ce ya samu labarin har yanzun ƴan ta'addan ba su bar yankin ba
  • Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan Kaduna, Mansur Hassan, ya ce a saurare shi, zai fara tattara bayanai kafin ya ce komai

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kaduna - Wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki kauyen Angwar Danko da ke mazabar Kakangi a karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna.

Rahotanni sun nuna cewa ƴan ta'addan sun tilasta wa wadanda gomman mutanen da suke ƙoƙarin yin garkuwa da su, su shiga daji.

Gwamna Uba Sani.
Yan bindiga sun tasa keyar gomman mutane zuwa cikin jeji a Kaduna Hoto: Senator Uba Sani Asali: Twitter

Daily Trust ta tattaro cewa ‘yan bindiga da yawa ne suka mamaye garin da misalin karfe 6 na yammacin ranar Laraba, inda suka buɗe wuta kan mai uwa da wabi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ganau sun bayyana cewa yanzu haka ƴan bindigan sun fara tafiya da mutanen kauyen maza da mata zuwa cikin daji.

Yahaya Musa Dan Salio, wakilin gundumar Kakangi a majalisar dokokin jihar ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya bayyana cewa har yanzu bai samu cikakken bayani ba dangane da adadin mutanen kauyen da aka sace amma ya tabbatar da cewa suna da yawa.

“Yanzu na samu kira daga yankin, inda aka sanar da ni cewa an yi garkuwa da mutane da dama.

"Ƴan bindigar sun kewaye kauyen, kuma a yanzu da muke magana suna can, suna kokarin tafiya da mutane zuwa cikin daji. Lamarin ya yi muni,” inji shi.

Dan Salio ya nuna damuwarsa kan faruwar lamarin inda ya ce akasarin wadanda harin ya rutsa da su maza ne kuma za a iya samun asarar rayuka.

Ya kuma jadddaa buƙatar tura ƙarin jami'an tsaro su tare hanyoyi domin daƙile yunƙurin ƴan bindigar.

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Mansur Hassan, ya ce zai tuntubi yankin domin jin cikakken bayani kafin ya yi magana.

Asali: Legit.ng

People are also reading