Home Back

Jamus ta cafke masu yi wa China leken asiri

dw.com 2024/5/19
Wata ma'aikaci da ke satar bayanai ta na'urar kwamfuta
Wata ma'aikaci da ke satar bayanai ta na'urar kwamfuta

Masu shigar da karar sun yi amannar cewa mutanen uku suna da hannu wajen ayyukan bincike da za su taimaka wa China ta fadada karfin tsaron ruwanta.

Karin bayani: Jamus ta kama masu yi wa Rasha leken asiri

'Yan sanda sun kama mutanen ne a  biranen Dusseldorf da Bad Homburg dake yammacin Jamus. Ana kuma binciken gidaje da wuraren ayyukan mutanen da ake zargi.

An bayyana cewa hukumomin China ne suka dauki nauyin ayyukan binciken da ake zargin mutanen da gudanarwa, to amma ya zuwa yanzu dai China bata ce uffan ba kan wannan batu.

Ko da a makon da ya gaba ma dai 'yan sandan Jamus sun kama wasu mutum biyu da aka zarga da yi wa Rasha leken asiri.

People are also reading