Tinubu Yana Kasar Waje Saboda Rashin Lafiya? Minista Ya Fadi Gaskiya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
FCT, Abuja - Gwamnatin tarayya ta ƙaryata raɗe-raɗin da ake ta yaɗawa dangane da rashin dawowar shugaban ƙasa Bola Tinubu gida Najeriya.
Gwamnatin tarayyar ta bayyana cewar lafiya ƙalau Shugaba Tinubu yake saɓanin jita-jitar da ke cewa yaje neman lafiya ne.
ƙaramin ministan lafiya da walwalar jama’a, Dr. Tunji Alausa ne ya bayyana hakan a wata hira da gidan talabijin na Channels tv a ranar Talata.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Shugaba Tinubu dai har yanzu bai dawo Najeriya ba kwanaki bayan kammala taron tattalin arziƙi na duniya da aka gudanar a ƙasar Saudiyya, lamarin da ya jawo cece-kuce kan inda ya tafi.
Sai dai, Tunji Alausa yayin da yake mayar da martani kan jita-jitar, ya ce Tinubu ba neman magani ya tafi ba ƙasar waje.
"Bari na gaya muku, muna samar da tsarin kiwon lafiya ga ƴan Najeriya ba shugaban ƙasa kaɗai ba. Muna da ƴan Najeriya 220m wannan shi ne abin da shugaban ƙasa yake so."
"Muna da shugaban ƙasa wanda yake da lafiya, mai ƙoshin lafiya sannan yana jagorantar ƙasar nan ta hanyar da ta dace."
"Shugaban ƙasa yana samun wani ɓangare na kula da lafiyarsa a Najeriya."
- Dr. Tunji Alausa
Ku kalli bidiyon a nan:
A wani labarin kuma, kun ji cewa fadar shugaban ƙasa ta bayyana lokacin dawowar shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu daga ƙasar waje.
Bayo Onanuga mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, ya bayyana cewa Shugaba Tinubu zai dawo gida Najeriya a ranar Laraba, 8 ga watan Mayun 2024.
Asali: Legit.ng