Ganduje: Yayin da Ake Cece-kuce, Abba Kabir Ya Fayyace Gaskiya Kan Kafa Kwamitin Bincike
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Kano - Gwamna Abba Kabir ya yi martani kan binciken tsohon gwamnan jihar, Dakta Abdullahi Umar Ganduje.
Gwamnan ya ce ko kadan babu bita da kullin siyasa kan binciken badakalar kadarorin gwamnatin jihar, cewar Daily Trust.
Abba ya bayyana haka ne yayin karbar bakwancin Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero a gidan gwamnati bayan ya kawo ziyarar gaisuwar sallah.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ya ce ya kafa kwamitin ne dokin tabbatar da gaskiya da kuma neman hanyar dakile rikicin siyasa a jihar da ya faru a baya.
Ya kuma sha alwashin cewa zai yi dukkan mai yiwuwa domin daukar mummunan mataki kan masu ingiza rikicin siyasa ko da kuwa daga wace jami'yya ce.
Tun farko a jawabinsa, Sarkin Kano ya ce sun zo gidan gwamnatin ne domin gaisuwar sallah ga gwamnan a yau Juma'a 12 ga watan Afrilu.
Sarkin ya yabawa gwamnan kan irin ayyukan alheri da ya kawo a jihar domin ci gaban al'umma, cewar rahoton New Telegraph.
Ya shawarci iyayen yara dasu tabbatar sun ba 'ya'yansu kulawa da tarbiyya domin dakile matsalar dabanci a siyasar jihar.
A baya, mun kawo muku labarin cewa wata kungiyar a jihar Kano ta ja kunnen Gwamna Abba Kabir kan binciken shugaban jam'iyyar APC, Dakta Abdullahi Ganduje.
Kungiyar mai suna Arewa Renaissance Front ta ce Ganduje bai tsoron komai saboda ayyukan alheri da ya yi a jihar.
Wannan na zuwa ne bayan Gwamna Abba Kabir ta kafa kwamitin bincike kan tsohon gwamnan jihar, Dakta Abdullahi Umar Ganduje.
Asali: Legit.ng