‘Bashi Bai Amfanar Talaka’, an Bukaci Bincike Yadda Najeriya Ke Kashe Bashin da Ta Ci
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Nigeria - Kungiyoyin na cigaba da tofa albarkacin baki kan sanarwar da gwamnati ta fitar a kan tarin bashi da aka samu na N121.67trn a cikin watanni uku.
A dalilin haka ne kungiyar SERAP ta bukaci Bankin Duniya ya binciki hukumomin Najeriya kan yadda suke kashe bashin da suka ciwo.
Jaridar Tribune ta ruwaito cewa SERAP ta ce akwai yiwuwar cewa bashin da ake ciwowa kasar bai amfanin talakawa.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Kungiyar SERAP ta ce ya kamata Bankin Duniya ya binciko yadda aka kashe bashin da aka ciwo a Najeriya tun daga 1999 har zuwa 2024.
SERAP ta ce binciken ya kamata ya haɗa tun daga gwamnatin tarayya har sauran jihohi 36 domin zargin karkatar da kudin da ake musu a tsawon shekaru.
A cikin takardar da mataimakin daraktan SERAP, Kolawole Oluwadare ya sanyawa hannu ya ce cikin shekaru an ciwo bashin $36b a Najeriya.
Kolawole Oluwadare ya ce babban abin takaici shi ne har yanzu talakawa ba su ga wata fa'ida daga bashin ba, rahoton Leadership.
Har ila yau Kolawole Oluwadare ya ce duk bashin da ke ciwo har yanzu sassa daban-daban na Najeriya ba su san ana gwamnati ba saboda ba su da abubuwan more rayuwa.
Ya ce har yanzu babu wutar lantarki wadatacciya a kasar kuma yan Najeriya sai kara shiga talauci suke yi.
A wani rahoton, kun ji cewa majalisar dattawa ta amincewa gwamnatin tarayya ta ranto $500m domin sanya mitar wuta a gidajen ‘yan Najeriya yayin da ake matsalar wuta.
Hukumar da ke lura da sayar da kadarorin gwamnati (BPE) ce za ta mika makudan kudin domin ta tabbatar da an sayo mitar da za a rarraba ga 'yan kasa.
Asali: Legit.ng