Home Back

'Idan dai Babu Wuta, Babu Biyan Sabon Kudin Lantarki', Minista ya zuga 'yan Najeriya

legit.ng 2024/5/17
  • Ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu ya shawarci yan Najeriya kan matakin da za su dauka a kan rashin wuta
  • Ministan ya ce ka da wanda ya biya sabon kudin wutar da bai sha ba yayin da ake fama da karancin wutar a fadin Najeriya
  • Adebayo Adelabu ya bayar da shawarar ne lokacin da ya bayyana gaban kwamitin majalisar dattawa kan wutar lantarki

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Abuja-Ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu ya umarci yan Najeriya da ka da su kuskura su biya kudin wutar da ba su sha ba.

Wannan na zuwa ne a dai-dai lokacin da yan Najeriya ke fama da matsanancin rashin wutar lantarki bayan an canza farashi.

Ana fama da matsalar wuta duk da karin kudin wutar da gwamnatin tarayya ya amince a yi
Ministan na ganin bai kamata yan Najeriya su biya kudin da ba su sha ba Hoto:Bayo Adelabu/Transmission Company of Nigeria Asali: Facebook

Ministan ya jaddada cewa duk kwastomomin da ke kan layin band A da B da aka yi wa alkawarin samun wutar awa 20, kuma ba sa samu, su rike kudinsu, kamar yadda Leadership News ta wallafa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce bai kamata yan Najeriya su biya sabon kudin wutar lantarki ba idan ba sa samun wuta.

Gwamnati za ta biya tallafin wutar lantarki

Ministan wutar lantarkin,wanda ya bayyana a gaban kwamitin majalisar dattawa kan wutar lantarki a Litinin dinnan ya ce gwamnati za ta biya tallafin wutar lantarki.

Ya kara da cewa ana bukatar akalla Dala biliyan 10 duk shekara na tsawon shekaru 10 kafin a iya farfado da sashen wutar lantarki a Najeriya, kamar yadda Punch News ta ruwaito.

Ministan na ganin wannan ba zai yiwu ba ganin girman kasafin da sashen ke bukata.

A bangaren tallafi kuma Minista Adebayo Adelabu ya ce idan ba a duba farashin wutar ba, gwamnatin za ta biya Naira Tiriliyan 2.9 na tallafi ga bangaren.

Ya ce gwamnati ta bijiro da sababbin matakan ceto bangaren wutar lantarki a kasar nan, har ma ya ce wahalar da ake sha yanzu ba za ta dore ba.

Gwamnati za ta yi gwanjon DISCOs

A baya kun ji cewa gwamnatin tarayya ta ce za ta sayar da wasu kamfanonin rarraba hasken wutar lantarki (DISCOS) guda biyar a kasar nan.

Wannan alwashi na zuwa ne a sa'ilin da hasken wutar ya yi karanci, kuma ake ci gaba da bukatar wutar saboda tsananin zafi.

Asali: Legit.ng

People are also reading