Home Back

Shugaban Masar ya tattauna batun tsagaita wuta azirin Gaza

dw.com 2024/8/23
Shugaba Abdel Fattah al-Sisi na kasar Masar
Shugaba Abdel Fattah al-Sisi na kasar Masar

A wannan Talata Shugaba Abdel Fattah al-Sisi na kasar Masar da William Burns daraktan hukumar leken asirin Amirka ta CIA sun tattauna kan batun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a yankin zirin Gaza na Falasdinu mai fama da yaki, tsakanin mayakan Hamas da dakarun Isra'ila.

Wata sanarwar fadar shugaban kasar ta Masar ta jaddada matakin kasar na watsi da ci gaba da yakin da ke faruwa. Ana sa ran wakilai daga bangarorin da ke rikicin da na masu shiga tsakani za su samar da mafita kan batun na tsagaita wuta.

People are also reading