Hukuma Ta Bukaci a Haddace Sabon Taken Najeriya Cikin Awanni 72, Ta Fadi Fa'idar Hakan
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
FCT, Abuja - Hukumar wayar da kan jama'a a Najeriya (NOA) ta bukaci a haddace sabon taken Najeriya cikin kwanaki uku.
NOA ta ba da wannan sanarwa musamman ga jami'anta da ke duka ƙananan hukumomi 774 a fadin Najeriya.
Ta bukace su da su iya sabon taken Najeriya da kuma haddace shi zuwa ranar 3 ga watan Yunin wannan shekara, cewar TheCable.
Hukumar ta ce jami'anta da ke cikin al'umma sune kashin bayan tabbatar da sabon taken Najeriya ya zauna a ƙasar, Peoples Gazette ta tattaro.
Ta ce tana hada kai da kungiyar malaman makaranta ta NUT domin tabbatar da ƙaƙaba taken Najeriya ga dalibai a makarantu baki daya.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Daraktan yada labarai na hukumar, Paul Odenyi ya ce hukumar ta himmatu wurin dabbaka sabon taken Najeriya a kasar.
"Muna farin ciki da shiga wani sabon babi na tarihi a Najeriya"
"Tabbas wannan sabon taken Najeriya zai kara karsashi da kishin kasa a zukatan ƴan Najeriya."
- Paul Odenyi
A wani labarin, kun ji cewa Shugaba Bola Tinubu ya tabbatar da dokar sauya taken Najeriya ga ƴan kasar.
Wannan rahoto ya kawo muku muhimman abubuwa shida da ya kamata ku sani game da sabon taken Najeriya da aka dawo da shi a yanzu.
Asali: Legit.ng