Home Back

Jam'iyyar ANC a Afirka ta Kudu ta kira babban gangami

dw.com 2024/7/1
Hoto: picture-alliance/B. Curtis

Jam'iyyar shugaban kasar Cyril Ramaphosa ta kira magoya bayanta ne a manyan filayen wasa na yankin Soweto da ke a birnin johannesburg a kokarin nemo tagomashinta, domin cike gibin da ta samu a zaben da ya gabata.

Zaben da za a yi shi a ranar Larabar da ke tafe ana ganin zai iya kasancewa zaben da jam'iyyar jagoran dimukuradiyya da ya kawo karshen wariyar launin fata wato Nelson Mandela za ta rasa samun rinjaye a cikinsa.

Masu nazarin harkokin siyasa a Afirka ta Kudun na ganin daga cikin wadanda za su iya yi wa ANCn lahani har da jam'iyyar da tsohon shugaban kasa Jacob Zuma ya kafa a baya-bayan nan.

People are also reading