Home Back

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Yi Alkawarin Magance Matsalar Ruwa Cikin Gaggawa

legit.ng 2024/5/19
  • Gwamna Inuwa Yahaya ya yi alkawarin magance matsalolin da suka dabaibaye harkar samar da ruwan sha a jihar Gombe
  • Gwamna ya yi alkawarin ne jiya Talata bayan matsalar ruwa ta yi ƙamari a fadin jihar sakamakon rashin wuta
  • Ya kuma bayyana lokacin da injiniyoyi da suke aikin za su kammala da kuma ranar da ruwa zai fara zuwa daga Dadinkowa

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Gombe - Gwamnan Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi alkawarin magance matsalar ruwan sha a fadin garin cikin gaggawa.

Rashin ruwa a Gombe
Rashin ruwa ya haifar da dogayen layuka a Gombe. Hoto: Shuaibu Salisu El-Diouf Asali: Facebook

Gwamnan ya yi bayanin ne biyo bayan karuwa da matsalar ruwan sha ta yi a kwaryar jihar Gombe.

Mai taimakawa gwmantin jihar a harkokin sadarwa Isma'ila Uba Misilli ya wallafa a shafinsa na Facebook cewa gwamnan ya damu matuka da halin da al'umma ke ciki.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yaushe za a magance matsalar ruwa?

Bayanai sun nuna cewa gwamna Inuwa Yahaya ya ce za a kawo karshen matsalar ruwan ne zuwa gobe Laraba, 1 ga watan Mayu.

Saboda haka ne ma ya umurci ma'aikatar samar da ruwan sha ta jihar da ta gaggauta daukan dukkan matakan da suka dace domin magance matsalar.

Me ya jawo matsalar ruwa a Gombe?

Gwamnatin ta koka a kan cewa matsalar ruwan ta faru ne sakamakon katsewar wutar lantarki bayan lalata layukan wuta a tsakanin Jos da Gombe.

Sun kara da cewa bayan an samu nasarar canja layi zuwa Bauchi sai iska mai karfi ta lalata wasu layukan wutan kuma.

A cewarsu hakan ne ya jawo ayyukan samar da ruwa daga Dadinkowa suka tsaya cak a fadin jihar.

Gwamnatin ta bada hakuri tare da yabawa al'ummar jihar bisa nuna juriya da suka nuna a cikin halin da suka samu kansu a ciki

An shiga matsalar ruwa a Arewa

A wani rahoton kuma, kun ji cewa matsalar ruwa ta yi katutu a mafi yawan garuruwan Arewacin Najeriya ciki harda Gombe, Kano, Yobe da Adamawa.

Matsalar ta jefa al'umma da dama cikin damuwa har ta fara kai wa da rashin samun gabatar da ibada cikin sauki.

Asali: Legit.ng

People are also reading