Home Back

Mataimakin Shugaban Kasar Malawi Ya Rasu Hatsarin Jirgin Sama

leadership.ng 2024/7/1
Mataimakin Shugaban Kasar Malawi Ya Rasu Hatsarin Jirgin Sama

Mataimakin shugaban kasar Malawi, Saulos Chilima ya rasu sakamakon hatsarin jirgin da ke dauke da shi ya yi a ranar Litinin.

Shugaban kasar Malawi, Lazarus Chikwera ya ce “jirgin nasa ya daki dutse” ne inda jirgin ya tarwatse kuma mista Chilima da duka wadanda ke cikin jirgin suka rasu.

An dai samu tarkacen jirgin ne a kusa da wani tsauni.

An dai kwashe awanni ana bincike domin gano jirgin saman da ke dauke da mataimakin shugaban kasar Malawi.

A ranar Litinin ne, wata sanarwa daga fadar shugaban kasar, ta bayyana cewar an daina jin duriyar jirgin saman mallakin Ma’aikatar Tsaron Malawi bayan da ya bar babbar birnin kasar, lilonge, a ranar Litinin da safe.

Shugaban kasar ya bayar da umarnin gudanar da aikin ceto bayan da jami’an sufurin jiragen sama suka gaza jin duriyar jirgin.

Kamata ya yi jirgin ya sauka a filin jirgin saman kasa da kasa na Mzuzu, da ke shiyyar arewacin kasar da misalin karfe 10 na safe.

Bayan da aka sanar da shi game da afkuwar lamarin, nan take shugaban kasar Lazarus Chakwera ya soke tafiyar da ya shirya yi zuwa tsibirin Bahamas.

People are also reading