Gwamna Radda Ya Samo Mafita Ga Gwamnati Kan Mafi Karancin Albashi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
Jihar Katsina - Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya bayyana cewa ya kamata a bar kowace gwamnatin jiha ta tsara mafi ƙarancin albashinta.
Gwamna Radda ya bayyana cewa a Najeriya ne kaɗai ake amfani da tsarin mafi ƙarancin albashi na bai ɗaya.
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin wata tattauna da gidan talabijin na TVC.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A halin yanzu a ƙasar nan, gwamnatin tarayya ce ke da ikon samar da mafi ƙarancin albashin da za a riƙa yin amfani da shi.
Ƙungiyoyin ƙwadago sun buƙaci a ƙarawa ma'aikata albashi biyo bayan cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi.
Yayin da gwamnatin tarayya ta yi tayin N62,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi, ƙungiyoyin ƙwadagon sun dage sai an biya N250,000.
Gwamna Dikko Radda ya yi nuni da cewa akwai kuskure a samar da mafi ƙarancin albashi wanda jihohi ba za su iya aiwatar da shi ba.
"A Najeriya ne kawai muke da mafi ƙarancin albashin ma'aikata iri ɗaya a dukkanin jihohi. A wasu ƙasashen, jihohi daban-daban suna da mafi ƙarancin albashin daban-daban bisa yadda za a su iya biya."
"Menene amfanin gwamnatin jiha ta amince za ta biya N100,000 idan ba za ta iya aiwatarwa ba."
- Dikko Umaru Radda
A wani labarin kuma, kun ji cewa Gwamna Dikko Umaru Radda na jihar Katsina ya gwangwaje ma’aikata da barka da sallah a faɗin jihar.
Gwamna Radda ya ba da kyautar N15,000 ga duka ma’aikatan jihar yayin da kuma ya ba su bashin N30,000 domin gudanar da bukukuwan salla cikin walwala.
Asali: Legit.ng