Home Back

Gwamna Radda Ya Samo Mafita Ga Gwamnati Kan Mafi Karancin Albashi

legit.ng 2024/7/2
  • A yayin ake ci gaba da taƙaddama tsakanin ƴan ƙwadago da gwamnatin tarayya kan batun mafi ƙarancin albashi, gwamnan Katsina ya samo mafita
  • Gwamna Dikko Umaru Radda ya yi kiran da a bar kowace jiha a ƙasar nan ta samar da mafi ƙarancin albashin da za ta iya biyan ma'aikatanta
  • Gwamnan ya nuna cewa kuskure ne a samar da mafi ƙarancin albashi na bai ɗaya wanda wasu jihohin ba za su iya aiwatarwa ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Katsina - Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya bayyana cewa ya kamata a bar kowace gwamnatin jiha ta tsara mafi ƙarancin albashinta.

Gwamna Radda ya bayyana cewa a Najeriya ne kaɗai ake amfani da tsarin mafi ƙarancin albashi na bai ɗaya.

Gwamna Dikko ya yi magana kan mafi karancin albashi
Gwamna Radda ya yi kira da a bar kowace jiha ta samar da mafi karancin albashinta Hoto: @dikko_radda Asali: Facebook

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin wata tattauna da gidan talabijin na TVC.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Taƙaddamar gwamnati da ƴan ƙwadago

A halin yanzu a ƙasar nan, gwamnatin tarayya ce ke da ikon samar da mafi ƙarancin albashin da za a riƙa yin amfani da shi.

Ƙungiyoyin ƙwadago sun buƙaci a ƙarawa ma'aikata albashi biyo bayan cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi.

Yayin da gwamnatin tarayya ta yi tayin N62,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi, ƙungiyoyin ƙwadagon sun dage sai an biya N250,000.

Me Radda ya ce kan mafi ƙarancin albashi?

Gwamna Dikko Radda ya yi nuni da cewa akwai kuskure a samar da mafi ƙarancin albashi wanda jihohi ba za su iya aiwatar da shi ba.

"A Najeriya ne kawai muke da mafi ƙarancin albashin ma'aikata iri ɗaya a dukkanin jihohi. A wasu ƙasashen, jihohi daban-daban suna da mafi ƙarancin albashin daban-daban bisa yadda za a su iya biya."
"Menene amfanin gwamnatin jiha ta amince za ta biya N100,000 idan ba za ta iya aiwatarwa ba."

- Dikko Umaru Radda

Gwamna Radda ya gwangwaje ma'aikata

A wani labarin kuma, kun ji cewa Gwamna Dikko Umaru Radda na jihar Katsina ya gwangwaje ma’aikata da barka da sallah a faɗin jihar.

Gwamna Radda ya ba da kyautar N15,000 ga duka ma’aikatan jihar yayin da kuma ya ba su bashin N30,000 domin gudanar da bukukuwan salla cikin walwala.

Asali: Legit.ng

People are also reading