Majalisar Dokokin Kano za ta ƙirƙiri Sarakuna masu daraja ta biyu a Kano
Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Dokokin Kano, Honorabul Lawal Hussaini ya bayyana cewa za a ƙirƙiri Sarakuna masu daraja ta biyu a Jihar Kano.
Gidan Radiyon Freedom da ke Kano ya ruwaito cewa: *Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Dokokin Kano Lawan Hussaini Chediyar ‘Yangurasa ya shaida wa Freedom Radio cewa za a ƙirƙiri ƙarin masarautu masu daraja ta biyu a Kano.
Ya ce gobe Juma’a ne zai gabatar da ƙudirin a Majalisar Dokokin Kano.
Shi ne dai Ɗan Majalisa wanda ya gabatar da ƙudirin soke dokar da gwamnatin Ganduje ta yi, wadda ta ƙirƙiro sabbin masarautu, wadda aka rushe a yau Alhamis.
Hakan na zuwa ne jim kaɗan bayan bayyana sake naɗa Sarki Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano baki ɗaya, bayan rushe sarakuna biyar da Ganduje ya ƙirƙira.