Abuja: Jerin Ma’aikatu da Hukomi 25 da Kamfanin AEDC Zai Datse Wa Wutar Lantarki
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Abuja - Kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja (AEDC) ya fitar da sunayen hukumomi da ma'aikatu 25 da suka yi fice wajen kin biyan kudin wutar lantarki.
Kamfanin rarraba wutar ya ce zai katse wutar dukkanin abokan huldarsa da suka gaza biyan basussukan su nan da ranar 3 ga Yuni.
Kamar yadda jaridar The Nation ta ruwaito, abokan huldar kamfanin sun hada da barikin sojojin kasa da na sojojin sama, gwamnatin jihar Kogi, gwamnatin jihar Neja da dai sauransu.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Duba sunayen hukumomi da ma'aikatu 25 da kamfanin zai datse wutar su idan suka gaza biyan kudin, kamar yadda jaridar The Cable ta tattara:
A wani labarin, mun ruwaito hukumar da ke kula da wutar lantarki ta Nijeriya, ta yi karin kudin wuta ga akalla anguwanni 481 da ke samun wutar ta awa 20 a rana.
Matakin da hukumar NERC ta dauka na kara farashin wutar lantarki ga abokan hulda na 'Band A' ya fuskanci suka daga masu ruwa da tsaki.
Asali: Legit.ng