Home Back

‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yansanda 4 A Katsina

leadership.ng 2 days ago
‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yansanda 4 A Katsina

Rundunar ‘yansandan Jihar Katsina, ta bayyana cewar wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun kashe jami’anta hudu a harin kwanton bauna da suka kai a jihar.

Mazauna garin Zandam na karamar hukumar Jibia sun shaida wa LEADERSHIP cewa maharan sun far wa dakarun ne a ranar Lahadi.

Kakakin ‘yansandan jihar, ASP Abubakar Sadik Aliyu, ya bayyana cewar ‘yansanda hudu ne suka rasa rayukansu kuma tuni ta tura karin dakaru zuwa wurin.

Irin wannan harin ba shi ne na farko ba a Jihar Katsina, inda ‘yan bindiga ke kashs jami’an tsaro.

A wasu lokuta har dakarun soji suke kai wa hari.

Sai dai a baya-bayan nan rundunar sojin Nijeriya na samun nasarar kawar da jiga-jigan ‘yan bindiga a Arewa Maso Yammacin Nijeiriya.

People are also reading