An Sake Tafka Babban Rashi Bayan Mutuwar Jarumin Fina-finai a Najeriya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Lagos - An sake tafka babban rashi bayan fitaccen jarumin fina-finan Nollywood, Zulu Adigwe ya riga mu gidan gaskiya.
An sanar da rasuwar marigayin a yammacin jiya Talata 23 ga watan Afrilun wannan shekara.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Mai shirya fina-finai a Nollywood, Stanley Nwoke shi ya tabbatar da haka a shafinsa na Instagram.
Stanley ya bayyana cewa har zuwa lokacin sanar da mutuwar marigayin ba a gano musabbabin mutuwar tasa ba.
"Ina mai bakin cikin sanar da ku cewa fitaccen jarumin fina-finan Nollywood, Zulu Adigwe ya rasu."
"Musabbabin mutuwar jarumin har yanzu ba a fayyace ba, Allah ya masa rahama."
Lokacin da ya ke kan kaifnsa, Adigwe ya yi shura a fina-finai kamar su 'Living in Bondage' da 'Breaking Free' da sauransu.
- Stanley Nwoke
Bayanai na biyo baya...
Asali: Legit.ng