Home Back

'Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga a Benin

dw.com 2024/5/19
Masu zanga-zanga a birnin Cotonou na kasar Benin dauke da kwalaye
Masu zanga-zanga a birnin Cotonou na kasar Benin dauke da kwalaye

Wakilin kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP ya bayyana cewa 'yan sanda sun tarwatsa wasu gungun mutanen da ke gudanar da zanga-zangar a babban birnin kasar.

Kazalika guda daga cikin masu zanga-zangar Ariane Assilamehou ta shaidawa AFP cewa 'ta zo ne domin shiga gangamin yaki da tsadar rayuwa, amma 'yan sanda sun hana su rawar-gaban hantsi wajen harbin su da barkonon tsohuwa.

Babbar kungiyar kwadagon kasar ta Benin CSA ta ce 'yan sanda sun yi awon-gaba da shugaban kungiyar Anselme Amoussou. 'Yan sanda sun ki cewa uffan dangane da wannan al'amari na murkushe masu zanga-zangar tsadar rayuwa a gwamnatin shugaba Patrice Talon.

People are also reading