Home Back

NLC Na Gudanar Da Zanga-zanga A Ofishin KEDCO Na Kano Kan Ƙarin Ƙuɗin Wutar Lantarki

leadership.ng 2024/6/18
Ƙungiyar Ƙwadago Ta NLC Na Zanga-zanga Kan Ƙarin Ƙudin Wutar Lantarki A Nijeriya

Ƙungiyar ƙwadago (NLC) ta ƙasa reshen jihar Kano ta gudanar da wata zazzafar zanga-zanga da safiyar yau Litinin a ofishin kamfanin rarraba wutar lantarki na KEDCO da kuma ofishin hukumar kula da wutar lantarki ta ƙasa (NERC) da ke Kano.

Sakataren NLC na jihar, Abbas Ibrahim, ya bayyana cewa; wannan matakin da suka dauka na zanga-zangar ya biyo bayan ƙarin kuɗin wutar lantarki da aka yi, wanda ƙungiyar ba za ta lamunta ba.

Ibrahim ya ce; ana gudanar da wannan zanga-zangar ne a duk jahohin Nijeriya baki ɗaya domin neman lallai a janye wannan ƙarin kuɗin wutar lantarki da aka yi, tare da mayar da farashin wutar kamar yadda yake a baya.

Sai dai kuma kamfanin na KEDCO har yanzu babu wata sanarwa ko martani da ya yi kan zanga-zangar. Watakila hakan na da nasaba da cewa matakin ƙarin kuɗin wutar ya faru ne a ƙasa baki ɗaya ba iya Kano ba.

Yanzu dai ido ya koma kan ministan wutar lantarki na ƙasa, Adebayo Adelabu, ko me zai ce game da kiraye-kirayen rage kuɗin wutar lantarkin da aka ƙara da kaso 300%.

People are also reading