Tsaro: Gwamatin Sokoto ta Tumbuke Hakimai 15 bisa Rashin Biyayya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Jihar Sokoto-Gwamnatin jihar Sakkwato ta sauke masu rike da sarautun gargajiya guda tara bisa laifuffukan hannu a cikin rashin tsaro da cinye filayen jama'a, da rashin biyayya ga gwamnati.
Hakiman da aka sauke sun hada da na Unguwar Lalle, da Yabo, da Wamakko, sai Tulluwa, Ilela, Dogon Daji, Kebbe, Alkammu da Giyawa, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
A sanarwar da Abubakar Bawa, mai magana da yawun gwamna Ahmed Aliyu, ya fitar, ya ce gwamnatin ta kori hakimai guda shida da tsohuwar gwamnatin jihar ta nada saboda al'umma ba sa sonsu.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Wadanda aka sauke sun hada da Marafan Tangaza, Sarkin Gabas, Kalambaina, Bunun Gongono, Sarkin Kudun 'yar Tsakkuwa, Sarkin Tambuwal da Sarkin Torankawa.
Gwamnatin na bincike hakiman garin Isa, Kuchi, Kilgori da Gagi.
Rahoton da Leadership News ta wallafa ya nuna ba dukkanin masu sarautun gargajiyar aka sauke daga mukamansu ba.
An sauyawa babban mashawarci a fadar Sarkin Musulmi, Sarkin Yakin Binji wuri zuwa Nabunkari, yayin da aka mayar da hakimin Sabon Birni zuwa Gatawa.
Su kuma hakiman da aka bari a mukamansu sun hada da shugaban Sokoto, Alhaji Aliyu Abubakar III, Barayar Zaki Alhaji Ibrahim Dauki Maccido, Sarkin Arewan Salame Abubakar Salame, da Sarkin Yamman Balle Aminu Bello.
Sauran sun hada da hakimin Sarkin Gabas Dandin Mahe Mahmoud Yabo, da Sarkin Gabas Ambarura Muntari Tukur Ambarura da Sarkin Gabas Rarah Malam Isa Rarah.
Gwamnatin ta ce an mayar da Sarkin Rafin Gumbi AbdulKadir Mujeli kujerarsa, yayin da aka tsare hakiman Tsaki da Asare.
Mun kawo mu ku yadda wani mai sharhi, Sani Shinkafa ya zargi sarakunan gargajiya da cewa suna da hannu cikin rashin tsaron da ke addabar jihar Zamfara.
Ya ce masu rike da sarautun gargajiya da jami'an tsaro, likitoci da masu safarar kwayoyi na amfana sosai da rashin tsaron da ake ciki.
Asali: Legit.ng