Home Back

Rikicin Masarauta: Aminu Ado Ya Daga Tuta A Fadar Nassarawa

leadership.ng 3 days ago
Rikicin Masarauta: Aminu Ado Ya Daga Tuta A Fadar Nassarawa

Yayin da ake tsaka da rikicin masarautar Kano, Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero ya daga tutar mulki a karamar fadar da ke Nassarawa.

Wannan yana nuna iko da Sarkin yake da shi a yanzu.

A bisa al’ada, tutar na zama ne a matsayin alamar iko, kuma daga ta na alamta cewa sarki yana cikin fada.

Wannan kuwa na zuwa ne duk da umarnin gwamnatin Kano ga Sarki Aminu ya fice daga fadar a yayin da ake ci gaba da dambarwar sarautar Kano.

Akan daga tutar ce da misalin karfe 6 na safe a kuma sauke ta 6 na yamma ko idan sarki ya yi bulaguron aiki.

Kano ta shiga rikicin masarauta tun bayan da gwamnatin jihar ta rushe masarautun Bichi, Karaye, Rano da Gaya wanda tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje ya kirkiro.

Rikicin na ci gaba da haifar da rudani yayin da Aminu Ado Bayero da Sarkin Kano na 14, Muhammdu Sanusi II kowa ke ci gaba da ikirarin shi ne Sarkin Kano.

People are also reading