InnalilLahi: An Shiga Ɗimuwa Bayan 'Yan Bindiga Sun Hallaka Fitaccen Basarake a Taraba
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Taraba - Wasu 'yan bindiga sun yi ajalin wani fitaccen basarake a jihar Taraba bayan kai mummunan farmaki.
Maharan sun bindige Abdulmutalib Nuhu da ke sarautar kauyen Sansani a karamar hukumar Gasol a jihar, cewar Leadership.
Lamarin ya faru ne a daren jiya Alhamis 19 ga watan Afrilu a yankin awanni kadan kafin gudanar da kasaitaccen bikin gargajiya a karamar hukumar Ibbi.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
'Yan bindigan sun durfafi kauyen Sansani da misalin karfe tara na dare inda suka wuce kai tsaye fadar Sarkin tare da hallaka shi, cewar Politics Nigeria.
Yayan marigayin mai suna, Nuhu Sansani ya ce maharan sun kawo farmakin ne da dare inda suka hallaka basaraken tare da tafiya da wayoyinsa.
"Su iso kauyen da misalin karfe tara na dare inda suka wuce kai tsaye fadar suka hallaka shi tare da ɗauke wayoyinsa guda biyu."
"Yayin da suke ficewa daga kauyen, sun ci karo da wani akan babur inda suka harbe shi har ya karye a kafa sannan suka yi tafiyarsu."
- Nuhu Sansani
Mukaddashin kakakin rundunar 'yan sanda a jihar, ASP James Lashen ya ce ya na kan hanyar zuwa ofishinsu ba shi da labarin harin 'yan bindigan.
"Ba ni da masaniya, ina kan hanyar zuwa ofis, idan na samu wani karin bayani zan sanar da ku."
- James Lashen
A wani labarin, kun ji cewa wasu 'yan mata uku sun rasa rayuwarsu yayin hatsarin jirgin ruwa a jihar Neja.
Lamarin ya faru yayin da 'yan matan suka kife a cikin kogi a kan hanyarsu ta zuwa gaisuwar salla a karshen mako.
Wani mai sana'ar su, ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce sun ceto wasu mata da direban amma sun tsamo gawarwakin matan uku.
Asali: Legit.ng