Sarki Muhammadu Sunusi II ya Jagoranci SallarJuma'a a Fadar Gwamnatin Kano
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Jihar Kano-Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sunusi II ya jagoranci sallar Juma'a a masallacin dake fadar gwamnatin Kano.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana cewa sabon sarkin ne zai jagorance su sallah jim kadan bayan tabbatar da shi a matsayin sabon sarkin Kano.
The Guardian ta wallafa cewa gwamnan ya shaidawa dandazon masoyan Sarkin cewa bayan ya idar da salla zai koma fadarsa.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya umarci dukkanin jami'an gwamnati da suka halarci taron nadin Malam Muhammadu Sunusi II da su tsaya su ji hudubar sabon Sarki.
BBC pidgin ta ruwaito cewa an nada Sarki Muhammadu Sunusi II ne duk da umarnin kotu da ya haramta hakan.
Amma a kalaman Gwamna Abba gida-gida:
"Ai ba sabon Sarki ba ne, dama kujerarsa ce ya dawo bayan ya bar ta na wucin gadi."
"Idan Allah Ya yadda idan muka gama wannan taro,masu girma hakimai, masu girma 'yan majalisa, masu girma shugabannin kananan hukumomi,da duk wadanda suka dace, ku zauna
"Sarkin mu adali, Sarkin mu mai ilimin addinin musulunci zai zo wanna masallaci na gidan gwamnati zai yi mana huduba, zai jagorance mu sallar Juma'a."
A kalamansa, sabon Sarkin Kano ya bayyana sake nada shi sarautar da bukata da addu'ar mutanen Kano da suka yi ba dare ba rana.
Mun kawo muku labarin cewa Gwamna Kano Abba Kabir Yusuf ya nada Malam Muhammadu Sunusi II a matsayin sabon sarkin Kano na 16.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya mikawa Malam Sanusi II takardar tabbatar masa da sarautar shekaru hudu bayan tsohuwar gwamnati ta tunbuke shi.
Asali: Legit.ng