Hukumar Shirya Jarabawa JAMB Ta Saki Sakamakon Jarabawar UTME 2024
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
FCT Abuja - Hukumar da ke shirya jarabawar share fagen shiga manyan makarantu (JAMB) ta saki sakamakon dukkan ɗaliban da suka zauna jarabawar a 2024.
Shugaban JAMB na ƙasa, Farfesa Ishaq Oloyede, ne sanar da sakin sakamakon jarabawar UTME a taron manema labarai a hedkwatar JAMB da ke Bwari a Abuja.
Jaridar Vanguard ta tattaro cewa an fara zama jarbawar ne a ranar Jumu'a, 19 ga watan Afrilu kuma an kammala a ranar Litinin 29 ga watan Afrilu, 2024.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A cewar rahoton Punch, JAMB ta yi jinkirin sakin sakamakon jarabawar ne domin ƙara nazari da bincike da tsefe sakamakon don kar a samu matsala.
Hukumar ta yanke shawarin ƙara kwanaki kafin fitar da sakamakon jarabawar domin tabbatar da gaskiya game da zargin wani ya zana ma wani da sauran laifukan satar amsa.
Karin bayani na nan tafe...
Asali: Legit.ng