Muhimman Bayanai 5 da Ba a Sani Ba a Kan Tarihin Ajiye Mabudin Dakin Ka’aba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Kasar Saudi Arabia - Gwamnatin kasar Saudiyya ta sanar da rasuwar Sheikh Saleh Al-Shaibi a yau Asabar.
Sheikh Saleh Al-Shaibi shi ne wanda yake rike da makullin ɗakin Ka'aba har zuwa rasuwarsa a yau.
A wannan rahoton, Legit ta tatttaro muku abubuwa 5 da ya kamata ku sani a kan ajiye makullin dakin Ka'aba wanda ya samo asali tsawon shekaru.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Jaridar Alarabiyya News ta wallafa cewa Ƙabilar Bani Shaiba ne ke da ikon ajiye makullin Ka'aba kamar yadda Annabi Muhammad (SAW) ya mallaka musu.
Hakan na nuni da cewa ƴan ƙabilar Shaibah ne suke da ikon lura da ayyukan kula da dakin Ka'aba tare da hadin gwiwar hukumomi.
Tun kafin zuwan addinin Musulunci dama 'yan ƙabilar Shaibah ne ke rike da makullin ɗakin Ka'aba kuma suke masa hidima.
Amma bayan Musulunci ya karbi garin Makka a shekara ta takwas bayan Hijira sai Annabi Muhammad (SAW) ya tabbatar musu da ajiyar makullin har abada.
Jaridar Saudi Gazette ta wallafa cewa sahabi Usman bin Ɗalha ne ya rike makullin ɗakin Ka'aba a zamanin Annabi (SAW).
Annabi (SAW) ya yi umurni da a damƙawa Usman bin Ɗalha makullin bayan an karɓe shi daga wajensa a lokacin da aka samu buɗe garin Makka.
A tsawon tarihi an samu mutane 109 da suka rike makullin Ka'aba wanda na ƙarshen su shi ne Sheikh Saleh Al-Shaibi.
Bayan rasuwar Sheikh Saleh Al-Shaibi a yau ana tsammanin hukumomi a kasar Saudiyya za su naɗa wanda zai cigaba da rike makullin daga iyalan gidan Usman bin Ɗalha (Allah ya kara yarda da shi).
Masu rike da makullin suna yin dukkan ayyuka da suka shafi kula da dakin Ka'aba ciki har da budewa da kulle dakin idan bukata ta taso.
Har ila yau, su ne masu wanke dakin da ake yi duk ranar 15 ga watan Muharram da sauran ayyukan da suka shafi tsaftace shi da canza masa riga.
A wani rahoton, kun ji cewa wani mahajjaci daga jihar Jigawa a Arewacin Najeriya ya nuna kyakkyawan hali yayin da ya tsinci jakar hannu ɗauke da maƙudan kudi a Madinah.
Alhaji Abba Saadu Limawa ya yi cigiya domin bai wa mai jakar kayansa amma ba a ga mai ita ba, don haka ya kai wa hukumar NAHCON.
Asali: Legit.ng