Kano: Ba Kamar Aminu Ado Ba, Sanusi II Ya Fadi Abin da Zai Kai Shi Kotu Kan Sarauta
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Kano - Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya magantu kan rigimar sarautar jihar bayan Aminu Ado ya shigar da kara kotu.
Sanusi II ya ce ko da an tsige shi a sarauta babu abin da zai sa ya je kotu sai dai idan an cire shi kan zargin da zai bata masa suna.
Mai Martaban ya bayyana haka ne yayin hira ta musamman da jaridar The Sun a yau Asabar 15 ga watan Yuni a Kano.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ya ce idan har aka cire shi da zargin badakala zai je kotu ne domin wanke kansa saboda mutuncinsa yafi masa komai.
"Na yi sarauta na tsawon shekaru shida, alhamdulillah, na yi abin da zan iya, dalilin da zai sa na je kotu shi ne idan aka cire ni kan zargin da zai batamin suna."
"Dalili kuwa shi ne babban abin da nake mutuntawa fiye da komai shi ne mutunci na."
"Idan har suka zarge ni da badalaka ko wani abu daban, da zan je kotu saboda wanke kai na, amma sun ce wai rashin biyayya ne."
- Muhammadu Sanusu II
A wani labarin, kun ji cewa Sarki Muhammadu Sanusi II ya soki Abdullahi Ganduje da neman lalata al'adun jihar Kano.
Sanusi II ya ce an shafe fiye da shekaru 1,000 da masarautun Kano amma babu wanda ya bukaci karin wasu.
Sarkin ya ce Abba Kabir ya gyara duka barnar da Ganduje ya tafka lokacin da yake rike da ragamar gwamnatin jihar.
Asali: Legit.ng