Atiku Abubakar ya Faɗi Hanya 1 da Za a Ceto Najeriya Daga Halin da ta Shiga
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Abuja- Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya nemi haɗin kan jam'iyyun siyasa domin ceto Najeriya daga ƙangin da mulkin APC ya jefa ta. Atiku Abubakar, wanda ya yi takarar shugabancin kasar nan a zaɓen 2023 ya bayyana haka ne ga hadakar magoya bayan PDP da suka ziyarce shi domin jaddada goyon bayansu.
A wani sako da mataimakin ɗan takarar kan kafafen yaɗa labarai, AbdulRasheed Shehu ya wallafa a shafinsa na facebook, shugaban haɗakar Anucha Katchy ya yaba da kishin ƙasar da Atiku Abubakar ke da shi. Ya ce ana sane da yadda tsohon mataimakin shugaban kasar ya jagoranci tawagar da ta yi dalilin yafewa Najeriya wasu basussuka da ake binta daga Paris Club.
Ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar ya bayyana cewa matasa da mata na daga wadanda ya fi kamata a tallafawa.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ya ce matuƙar ya zama shugaban Najeriya, kaso 70% na mukaman gwamnati na matasa ne, yayin da zai bayar da $10bn ga masu kanana da matsakaitan sana'o'in mata zalla.
Sai dai Atiku Abubakar ya ƙara da cewa hakan ba zai tabbata ba sai an yi haɗaka mai ƙarfi domin kawar da APC daga mulkin Najeriya.
Jagoran PDP ya kuma bayyana farin ciki matuka da hadakar kungiyar ta ziyarce shi, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na X.
A wani labarin kun ji cewa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya musanta cewa Bola Tinubu ne ya cicciɓa shi a siyasar kasar nan.
Ya ce hasali ma shi ne ya yi faɗi tashin ceto siyasar Tinubu har ya iya zama gwamna a jihar Legas, don ba dan shi ba, da siyasar Tinubu ta zo ƙarshe.
Asali: Legit.ng