Zargin Ta’addanci: Kotu Ta Sallami Shugaban Miyetti Allah Bayan Wata 4 a Tsare
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Abuja - Wata babbar kotun tarayya ta sallami shugaban Miyetti Allah Kautal Kore, Alhaji Bello Bodejo daga tuhumar da gwamnatin tarayya ke yi masa na ta’addanci.
Mai shari’a Inyang Ekwo, a wani dan takaitaccen hukunci, ya sallami Bodejo bayan da lauyar gwamnati, Aderonke Imana ta gabatar da bukatar a janye tuhumar da ake masa.
A zaman shari'ar da aka ci gaba da yi a ranar Laraba, Imana ta sanar da kotun cewa tana da bukatar da za ta gabatar ta baki, in ji rahoton Channels TV.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Lauyar ta ce bukatar ta kasance a karkashin sashe na 108 na dokar kula da shari’a ta laifuffuka (ACJA), da aka yi a 2015.
Ta ce bukatar ta na da nasaba da karfin ikon babban lauyan tarayya AGF da ya samu a karkashin sashe na 174 na kundin tsarin mulkin 1999 (wadda aka sabunta).
Jaridar The Cable ta ruwaito Imana ta kara da cewa babban lauyan gwamnatin tarayya ya umarce ta da ta janye tuhumar da ake yi wa wanda ake kara a bisa doron adalci na shari'a.
Tawagar lauyoyin Bodejo ba su yi adawa da wannan bukatar ta Imana ba.
A cikin hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Inyang Ekwo ya ce:
“Bayan duba wannan bukatar, kotu ta ba da umarni a saki wanda ake tuhuma. Wannan shi ne umarnin wannan kotun."
Tun da fari, mun ruwaito jami'an tsaro sun kama Bodejo a ranar 23 ga watan Janairu a ofishin Miyetti Allah da ke karamar hukumar Karu a jihar Nasarawa.
An kama Bodejo ne biyo bayan kaddamar da kungiyar ‘yan banga ta Fulani a jihar, abin da gwamnati ta kira barazana ga tsaron kasa.
Asali: Legit.ng