Zaman Lafiya: Rundunar Sojoji Ta Bude Kofa Domin Yin Sulhu da ’Yan Bindiga
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Jihar Bauchi - Babban hafsun dakarun Najeriya Laftanal Janar Taoreed Lagbaja ya yi kira na musamman ga 'yan bindiga.
Laftanal Janar Taoreed Lagbaja ya bayyana hanyoyin da yan bindigar ya kamata su bi maimakon daukar makami.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa hafsun ya yi kiran ne a jiya Laraba yayin da ya kai ziyarar aiki a jihar Bauchi.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Laftanal Janar Taoreed Lagbaja ya ce ya kamata yan bindiga su tuba sun nemi tattaunawa da hukumomin Najeriya maimakon daukar makami.
Hafsun sojojin ya kara da cewa dukkan wanda ya ji an yi masa ba daidai ba, kamata ya yi ya nemi hanyar warware matsalar ba ta yaki da kasa ba.
Ya kara da cewa matukar babu zaman lafiya to dukkan abin da suke nema a wajen gwamnati ba lallai su samu ba, rahoton This Day.
Babban hafsun ya yi kira ga daukacin sojojin Najeriya kan cigaba da aiki domin bayar da tsaro a kasa baki daya.
Laftanal Janar Taoreed Lagbaja ya ce suna sane da dukkan matsalolin da dakarun rundunar ke fuskanta kuma suna ƙoƙarin daukan mataki.
Ya ce akwai matsalolin karin matsayi da samun albashi a kan lokaci wanda a yanzu haka ana ƙoƙarin magancesu.
A wani rahoton, kun ji cewa rundunar 'yan sandan Najeriya reshen jihar Bauchi ta cafke babban ɓarawo da ake zargin ya fitini al'umma da sace-sace.
Mutumin da ake zargi mai suna Glory Samuel ya sace makudan kudi da kayayyaki na miliyoyin kudi daga mutane da dama a jihar Bauchi.
Asali: Legit.ng