Rudin Soyayya: Rundunar Sojin Najeriya Ta Tabbatar da Jami’inta Ya Kashe Mace Mai Ciki
FCT, Abuja - Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da kisan wata mata da wani jami’inta ya yi a barikinta da ke jihar Enugu a yankin Kudu maso Gabashin Najeriya.
A makon da ya gabata ne aka samu rahoton cewa, Muhammad Adamu, wanda aka ce tubabben dan Boko Haram ne da ya shiga aikin soja ya kashe wata mata a barikin Sojan Najeriya na 82 da ke jihar.
Matar mai suna Hauwakulu Tabra, an ce budurwar Adamu ce. An ce tana dauke cikin da wani ya yi mata, wanda hakan ya fusata sojan, Premium Times ta ruwaito.
Da yake martani kan lamarin a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, kakakin rundunar, Onyema Nwachukwu, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an kama Adamu tare da tuhumarsa da aikata kisan kai.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Nwachukwu, ya ce ana zarfin Adamu da kashe matar ne a daren Alhamis kuma an gano gawarta a cikin harabar barikin a ranar Juma’a.
A cewarsa:
“Bincike na farko ya nuna cewa sojan ne ya kashe marigayi Hauwakulu Tabra, wanda a yanzu haka yake tsare don ci gaba da bincike tare da gano dalilin da ya sa ya aikata hakan.”
Sai dai, kakakin rundunar ya musanta ikirarin cewa Adamu dan Boko Haram ne da ya tuba, rahoton The Guardian.
Daga nan, ya mika sakon ta’aziyya ga iyalan Hauwakulu tare da bayyana jimamin abin da ya faru.
Kakakin ya kuma tabbatarwa ‘yan Najeriya cewa za a yi adalci a lamarin domin rundunar ba za ta lamunci duk wani dabi’a ta rashin da’a a cikin jami’anta ba.
A bangare guda, wani soja mai suna Egitanghan G. ya bayyana cewa za su dauki fansa kan kisan sojoji da aka yi a jihar Delta.
Sojan wanda shi ma ya fito daga jihar Delta ya ce abin takaici ne yadda wasu ke munanan kalamai ga sojojin da suka mutu.
Egitanghan ya nuna damuwa kan yadda abin ya faru duk da sadaukar da rayukansu da suke yi wurin kare kasar.
Asali: Legit.ng