Samoa: Gwamnati Ta Magantu Kan Ikirarin ’Yan Arewa Za Su Guji Tinubu a 2027
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
FCT, Abuja - Malaman Musulunci da dama a Arewa sun caccaki Bola Tinubu kan yarjejeniyar Samoa da aka sanyawa hannu.
Hakan ya biyo bayan sanya hannu a yarjrjniyar da wasu ke zargin akwai auren jinsi a ciki da ya saba addinin Musulunci da Kiristanci.
Hadimin Bola Tinubu a bangaren yada labarai, Dada Olusegun ya yi tsokaci kan lamarin inda ya wallafa a shafinsa na X.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Olusegun ya ce ba kamar yadda ake yadawa ba 'yan Arewa ba su da matsala da Tinubu a zaben 2027 da ke tafe.
Ya ce bai kamata wasu masu mugun nufi suna ikararin cewa 'yan Arewa za su juya baya ga Tinubu ba lokacin zabe.
Har ila yau, Olusegun ya ce har yanzu Bola Tinubu yana da goyon baya a Arewa kuma shi za su sake zaba a 2027 kamar yadda suka yi a 2023.
"Don Allah mu bar yada abin da bamu da masaniya a kai musamman wurin yin jam'i a maganganunmu."
"Yan Arewa ba su da matsala da Bola Tinubu, wasu masu mugun nufi ne da ke goyon bayan Alhaji Koojoli da muka kayar a 2023."
"Mafi yawan 'yan Arewa sun zabi Tinubu a zaben 2023 a kansa, kuma haka za su sake yi a zaben 2027 mai zuwa."
- Dada Olusegun
Kun ji cewa Gwamnatin Tarayya za ta dauki mataki kan rahoton Samoa da ake yadawa wanda ya sha bam-ban da abin da ta sanyawa hannu.
Gwamnatin Bola Tinubu ta ce za ta dauki matakin shari'a musamman kan Daily Trust saboda yawan kawo rahotanni marasa inganci.
Asali: Legit.ng