‘Daɗi Zai Biyo Baya’ Masana Sun Fadi Dalilin Goyon Bayan Tsare Tsaren Tinubu
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Nigeria - Tun farkon fara mulki shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya fara kirkiro tsare-tsaren da suka jefa al'umma cikin tasko.
Duk da kokarin da gwamnatin ta yi wajen bayyanawa yan Najeriya cewa ta dauki matakan ne domin inganta kasar hakan bai yi tasiri ba.
Wani masani ya tabbatar wa jaridar the Cable cewa matakan da gwamnatin ta dauka za su kai Najeriya kan tudun tsira.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Cikin tsare-tsare masu tsauri da Tinubu ya kawo akwai cire tallafin man fetur da ya yi a ranar 29 ga watan Mayun shekarar 2023.
Haka zalika a ranar 3 ga watan Afrilu shugaban kasar ya kara kudin wutar lantarki ga yan layin Band A.
Wani masanin tattalin arziki, Muda Yusuf ya ce duk da cewa tsare-tsaren sun haifar da wahalar rayuwa ga talakawa amma suna da amfani.
Muda Yusuf ya ce dole ne yan Najeriya su kara hakuri da juriya domin tabbatar da tsare-tsaren sun kawo cigaba a nan gaba kadan.
Duk da cewa masanin ya goyi bayan gwamnatin, ya ce dole ta saka gaggawa wajen daukan matakan da za su rage radadin da tsare-tsaren suka jawo.
Ya ce shekarar farko da fara gyaran an sha wahala sosai saboda haka ya kamata a rika kawo dauki da wuri.
A wani rahoton, kun ji cewa Muhammadu Buhari ya taya shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu murnar cika shekara ɗaya a kan madafun iko a Najeriya.
Tsohon shugaban ƙasar ya yi kira ga ƴan Najeriya su goyi bayan gwamnatin Tinubu a koƙarinta na kawo ci gaban ƙasa a Najeriya.
Asali: Legit.ng