Home Back

Katsina: Ƴan Bindiga Sun Farmaki GRA, Sun Sace Farfesa Da Wani Lakcara a Jami'ar Tarayya

legit.ng 2024/7/3
  • Wasu lakcarori biyu a Jami'ar Tarayya a Dutsinma sun gamu da iftila'i bayan ƴan bindiga sun yi awon gaba da su a jihar Katsina
  • Lamarin ya faru ne da safiyar jiya Litinin 3 ga watan Yuni a karamar hukumar Dutsinma da ke jihar a Arewacin Najeriya
  • Wadanda abin ya shafa sun hada da Farfesa Richard Kyaram da kuma ɗansa mai suna Solomon da wani Dakta Hamza

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Katsina - Ƴan bindiga sun yi garkuwa da lakcarori a Jami'ar Tarayya da ke Duntsinma a jihar Katsina.

Miyagun sun sace lakcarori biyu tare da wani mutum guda da safiyar ranar Litinin 3 ga watan Yuni a jihar.

The Guardian ta tattaro cewa maharan sun sace Farfesa Richard Kyaram da ɗansa mai suna Solomon da kuma wani Dakta Hamza.

Wadanda aka sacen suna rayuwa ne a yankin GRA da ke Dutsinma inda maharan suka farmaki yankin da muggan makamai.

Wata majiya ta tabbatar da cewa maharan sun bi gida-gida inda suke kwacen waya da kudi da sauran kayayyaki masu amfani.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Daga bisani an fitar da wadanda aka sacen daga gidajensu inda aka tafi da su wani wuri da ba a sani ba."

- Cewar majiyar

Karin bayani na tafe....

Asali: Legit.ng

People are also reading