Home Back

Wata Sabuwa: KEDCO Ta Yanke Wutar Jami’ar Dangote Da Ke Kano

leadership.ng 2 days ago
Wata Sabuwa: KEDCO Ta Yanke Wutar Jami’ar Dangote Da Ke Kano 

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano da Jigawa da Katsina (KEDCO) ya katse wutan lantarki ga Jami’ar Aliko Dangote da ke Wudil, saboda basussukan da ake binta da ya kai har Naira miliyan ₦248m.

Alhaji Abubakar Yusuf, Manajan Daraktan KEDCO ne ya bayyana haka a wata tattaunawa ta wayar tarho da Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya, a yau Litinin, Naira miliyan ₦20m ne kacal jami’ar ta iya biya a cikin bashin.

Yusuf ya bayyana cewa KEDCO ba ta da wata mafita illa ɗaukar wannan tsattsauran mataki, inda ya jaddada mahimmancin jami’ar na biya kuɗin da ya kamata kafin a dawo da wutar lantarki.

Ya nanata matsayin kamfanin na cewa ba tare da biyan kudi ba, jami’ar za ta ci gaba da zama cikin duhu.

People are also reading