Home Back

Bayan Rigimar Aurar da Marayu a Niger, Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Auren Mata 105 a Zamfara

legit.ng 2024/10/6
  • Yayin da ta'addanci ya yi ajalin iyaye a jihar Zamfara, dan Majalisar Tarayya ya tallafawa marayu a jihar
  • Abdulmalik Zubairu da ke wakiltar Bungudu/Maru ya dauki nauyin auren mata marayu 105 wadanda iyayensu suka rasa rayukansu
  • Ɗan Majalisar ya ce ya yi hakan ne domin dauke musu nauyin wahalar hidimar aure ganin cewa ba su da iyaye

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Zamfara - Dan Majalisar Tarayya daga jihar Zamfara ya dauki nauyin aurar da mata marayu 105 a jihar.

Hon. Abdulmalik Zubairu da ke wakiltar mazabar Bungudu/Maru ya dauki matakin domin tallafawa matan wadanda ƴan bindiga suka hallaka Iyayensu.

Abdulmalik ya bayyana haka ne bayan daura auren da Sheikh Liman Musa Kura ya jagoranta a garin Bungudu, kamar yadda ya tabbatar a shafin Facebook.

Ɗan Majalisar ya ce ya yi hakan ne domin rage musu dawainiya ganin cewa iyayensu sun rasu.

Ya ce a Musulunci iyaye ne ke da alhakin daukar nauyin auren ƴaƴansu amma tun da marayu ne ya dauke musu wannan wahalar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Har ila yau, Abdulmalik ya ce ya sayi gadaje da kujeru da sauran kayayyakin daki ga ma'auratan domin bikin cika shekara daya a Majalisa.

Daga bisani ya tallafawa ma'auratan da N100,000 da kuma N50,000 domin kula da kansu bayan sun yi aure.

Auren marayu ya jawo kace-nace a Niger

Kun ji cewa Kakakin Majalisar jihar Niger ya dauki nauyin auren mata marayu wanda ya jawo cece-kuce a fadin Najeriya.

Kakakin Majalisar ya dauki nauyin auren wasu mata marayu 100 inda Ministar mata, Uju Kennedy-Ohanenye ta maka shi a kotu kan haka.

Kennedy-Ohanenye ta ce hakan ya saba ka'ida inda ta bukaci koya musu sana'o'i madadin daura musu aure a wannan lokaci.

Asali: Legit.ng

People are also reading