Home Back

Katsina: An Kama Mutum 2 da Hannu a Sace Mahaifiyar Dauda Kahutu Rarara

legit.ng 2 days ago
  • Ƴan sanda sun kama wasu mutum biyu bisa zarginsu da hannu a garkuwa da mahaifiyar fitaccen mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara
  • Jami'in hulɗa da jama'a na rundunar ƴan sandan Katsina, ASP Abubakar Sadiq ya ce yanzu haka suna kan bincike don ceto dattijuwar
  • Wasu ƴan bindiga sun shiga gidan Rarara da ke mahaifarsa Kahutu a ƙaramar hukumar Ɗanja, suka tafi da mahaifiyarsa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Katsina - Rundunar ƴan sanda ta cafke mutum da ake zargin suna da hannu a sace mahaifiyar fitaccen mawanin siyasa, Dauda Adamu Kahutu Rarara.

Jami'in hulɗa da jama'a na rundunar ƴan sandan jihar Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ne y bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar yau Jumu'a.

Dauda Kahutu Rarara.
'Yan sanda sun kama mutum 2 da zargin suna da hannu a sace mahaifiyar Rarara Hoto: Dauda Kahutu Rarara Asali: Facebook

Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, ASP Abubakar ya ce yanzu haka waɗanda ake zargin suna hannun jami'ai ana ci gaba da bincike a kansu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Ofishin ƴan sanda na Ɗanja ya samu rahoton cewa masu garkuwa sun shiga gidan Hajiya Halima Adamu da ke garin Kahutu da misalin ƙarfe 1:30 na daren yau Jumu'a, suka tafi da ita.
"Nan take jami'an ƴan sanda suka nufi wurin da lamarin ya faru da niyyar kama masu hannu a harin gami da ceto matar cikin ƙoshin lafiya.
"A binciken da suka yi ne ƴan sandan suka kama mutum biyu da ake zargi, a halin yanzu muna kan aiki za mu sake fitar da bayanai a lokacin daya dace."

- ASP Abubakar Sadiq Aliyu.

Rarara dai fitaccen mawakin siyasa kuma ya taka rawa wajen tallafa takarar shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu musamman a garuruwan Hausawa.

Dauda Kahutu ya riƙe muƙamin shugabam mawakan shugaban ƙasa a lokacin muƙkin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari.

A ɗazu dai kwamishinan tsaro na jihar Katsina, Nasiru Mu'azu ya ce ƴan bindiga sun bi ta bayan gida ba tare da kowa ya sani ba, sun sace mahaifiyar Rarara a Kahutu

A rahoton The Nation, ya ce an tura ƙarin jami'an tsaro domin su bi sawun maharan da nufin ceto dattijuwar.

Asali: Legit.ng

People are also reading