Home Back

Spain da Ireland da Norway sun amince da zaman Falasdinu

dw.com 2024/6/29
Hoto: Rebecca Ritters/DW

A Talatar nan ce kasashen Spain da Ireland da  kuma Norway suka amince da Falasdinu a matsayin 'yantacciyar kasa mai cin gashin kanta a hukumance, lamarin da ya fusata Isra'ila.

Tun a makon da ya gabata ne dai kasashen uku suka tsayar da Talatar nan a matsayin ranar da za su sanar da wannan mataki a hukumance, wanda ya janyo musu martani ma zafi daga Isra'ila.

Ministan harkokin wajen Spain Jose Manuel Albares, ya ce sanarwar da kasashen uku suka fitar ta jaddada aniyarsu ta amincewa da 'yancin Falasdinawan, kuma ita ce matsayarsu a ko yaushe.

People are also reading