Home Back

An Dauki Mataki Kan Dan Sandan da Aka Nadi Bidiyonsa Ya Na Karbar ‘Na Goro’ a Imo

legit.ng 2024/7/1
  • Rundunar ‘yan sandan jihar Imo ta hukunta wani jami’anta mai suna Sifeta Isong Osudueh da aka nadi bidiyonsa yana karbar na goro
  • Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Henry Okoye, ya ce an ragewa Sifeta Isong matsayi saboda ladabtarwa
  • A ranar 26 ga watan Mayu ne aka yada bidiyon dan sandan yana karbar cin hanci daga hannu direbobi a hanyar Owerri zuwa Onitsha

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Jihar Imo - Rundunar ‘yan sandan jihar Imo ta ce ta dauki mataki kan jami’anta mai suna Sifeta Isong Osudueh da aka nadi bidiyonsa yana karbar cin hanci.

Rundunar ta ce ta rage wa Sifeta Isong matsayi saboda karbar 'na goro' hannu masu ababen hawa a kan hanyar Owerri zuwa Onitsha.

An dauki mataki kan dan sandan da aka kama yana karbar cin hanci a Imo
Rundunar 'yan sandan Imo ta hukunta jami'inta da aka kama yana karbar cin hanci. Hoto: @chekwube_henry Asali: Twitter

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Henry Okoye, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na X a ranar Litinin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An rage wa dan sanda matsayi

Bidiyon da ya bazu a ranar Litinin, ya nuna jami’in yana karbar kudi daga hannun direbobin da ke wucewa ta titin daya ke gudanar da bincike.

Ana kuma iya ganin shi yana mika canji ga wasu direbobin a duk lokacin da bukatar hakan ta taso.

A cewar sanarwar, an ragewa Osudueh, wanda ke aiki a sashin yaki da ta’addanci a Owerri matsayi bayan ya fuskanci hukuncin ladabtarwa.

Bidiyon dan sanda yana karbar na goro

A lokaci guda kuma, an baiwa jami'in da ke sa ido kan dan sandan takardar tuhuma sahoda rashin kulawa da da'ar jami'an da ke karkashinsa.

Wani mutum mai suna @ChuksEricE ne ya wallafa bidiyon dan sandan yana karbar 'na goro' a shafinsa na X.

Kalli bidiyon a kasa:

Masarautar Kano: Kotu ta ba 'yan sanda umarni

A wani labarin, mun ruwaito cewa wata babbar kotun jihar Kano ta ba 'yan sanda umarnin fitar da sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero daga fadar Nassarawa.

Haka zalika, kotun ta dakatar da tsofaffin sarakunan Kano biyar daga bayyana kansu a matsayin sarakuna biyo bayan karar da gwamnatin jihar ta shigar a kotun.

Asali: Legit.ng

People are also reading