Riba Biyu: Za a Mayarwa Alhazan Jihar Kaduna Kudi, Wasu Za Su Samu Canjin $50
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Kaduna - Hukumar kula da jin dadin alhazai ta jihar Kaduna ta bayyana aniyarta na mayarwa da alhazan jihar da suka biya kudin aikin hajjin bana ta hukumar wani kaso na kudin layyarsu.
Shugaban kwamitin hadaya na hukumar, AVM Muhammad Dabo mai ritaya da ya bayyana haka, ya ce za a bayar da $50 ga alhazai 700 da suka kamala aikin hajjin bana.
Nigerian Tribune ta wallafa cewa hukumar ta dauki mayar da kudin ne saboda an samu ragi daga kamfanin da ya yanka dabbobin layyarsu a Saudiyya.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Shugaban kwamitin hadaya na hukumar jin dadin alhazan jihar Kaduna, AVM Muhammad Dabo mai ritaya ya ce alhazai 700 cikin 1,357 za a bawa wani kaso na kudin yankansu.
Rahotanni sun ce gudun ka da su damfari mahajjatan ya sa aka nemi kamfanin da zai taimaka wajen hadayar alhazan saboda muhimmancinsa ga cikar ibadar hajji.
AVM Muhammad Dabo mai ritaya ya ce kamfanin farko da su ka tuntuba ya nemi N200,000 kudin hadayar, daga baya aka samu wani da yanka kowane rago kan riyal 375, kamar yadda Daily Nigerian ta wallafa..
A wani labarin kun ji cewa hukumar alhazai ta kasa (NAHCON) ta umarci musulmin Najeriya da ka da su dauko ruwan zam-zam daga kasa mai tsarki. Shugaban kula da jigila na hukumar, Muhammad Sanda ne ya bayar da umarnin a Makkah yayin da ake shirye-shiryen dawowar alhazan Najeriya gida bayan sauke farali.
Asali: Legit.ng