Za A Fara Ɗaure Mazinata Da Masu Zaman Dadiro A Gidan Yari A Indonesiya
Indonesiya - Za a fara hukunta mazinata, inda za a iya yanke musu hukuncin daurin tsawon shekara daya ga duk wanda aka samu da laifin, rahoton Reuters.
Ana fatan majalisar kasar za ta amince da sabbin dokokin a watan Disambar shekarar 2022.
DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar
Wasu ‘yan bindiga sun kai hari a wani masallaci a jihar Delta, inda da dama suka jikkata
Wasu abubuwa da ke kunshe cikin sabbin dokokin sun hada da:
A wani hira da ya yi da Reuters, mataimakin ministan shari'a na kasar, Edward Omar Sharif Hiariej, ya ce dokokin an yi su ne bisa tsarin 'al'adun Indonesia'.
An yi watsi da wani yunkurin da aka yi a baya na zartar da sabon kundin laifukan a 2019, a yayin da shugaban kasar Indonesiya Joko Widodo , wanda aka fi sani da Jokowi, ya ce damuwa da al'umma suka nuna kan wasu sassan.
A lokacin, Jakarta Post ta ruwaito cewa majalisar dokokin Indonesia ta fuskanci mummunan martani game da wasu abubuwa masu rikitarwa a cikin dokar da aka gabatar wanda zai haramta abubuwa da ake yi wa kallon ba laifi bane yayin da yake barazana ga 'yancin jama'a na bayyana ra'ayinsu, da sirri.
Wata sabuwa: CAN ta zargi wata hukuma da cinye kudin hajjin kiristoci a kasar nan
Sai dai kuma, kwanaki hudu kafin a zartar da daftarin kudirin, Jokowi ya dakatar da shari’ar.
Wani mutum na asalin kasar Indonesiya da ke aiki a majalisar malamai na garin Aceh ya shiga hannun hukuma bayan samunsa da laifin zina.
Mutumin mai suna Mukhlis ibn Muhammad dan shekara 28 yana cikin wadanda ke dabbaka shari'ar musulunci a garin na Aceh, BBC Hausa ta rahoto.
Asali: Legit.ng