Home Back

Kungiyar IS ta kaddamar da hare-haren ta'addanci a Kwango

dw.com 2024/6/26
Wani tsohon hoton 'yan tawayen M23 dauke da makamai a Jamhuriyar Dimukradiyyar Kwango
Wani tsohon hoton 'yan tawayen M23 dauke da makamai a Jamhuriyar Dimukradiyyar Kwango

A wannan mako kadai kungiyar IS ta halaka fararen hula 29, inda suka yiwa wasu fararen hula kisan gilla a wani kauye da ke kusa da Masau a Kivu, kamar yadda guda daga cikin shugabannin al'umma na yankin Mr. Kambale Gerve, ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Jamus na dpa.

Karin bayani: Kwango: Sabon rikici a arewacin Kivu 

Hukumar bada agajin gaggawa ta Red Cross ta ce sun yi nasarar kwaso gawarwaki 60 daga yankin, yayinda da wasu kuma ke can a warwatse akan tituna, kasancewar yankin na da hadarin shiga.

Karin bayani:  Kwango: Fada ya barke a Arewacin Kivu

Gerve, ya kuma kara da cewa "yan tawayen Allied Democratic Forces (ADF) na kasar Uganda da suka kulla kawance da kungiyar IS a 2019, sune suka kai harin na ta'addanci.

People are also reading