Home Back

Kasar Benin ta kama wasu 'yan Jamhuriyar Nijar

dw.com 2024/7/1
Jami'an tsaro a birnin Cotonou
Jami'an tsaro a birnin Cotonou

Kamen 'yan Nijar din da aka yi a tashar Seme-Kpodji, ya faru bayan zargin biyu daga cikin su da yi wa sojojin Nijar aiki mai kama da na leken asiri.

Wannan dai ya zo ne yayin da alakar diflomasiyya tsakanin Nijar da Jamhuriyar Benin da ke makwabtaka da juna ke kara tsami.

Bayan juyin mulki na watan Yulin bara a Nijar, kasashe makwabta sun rufe iyakokinsu da kasar, amma daga bisani Benin ta bude tata.

Sai dai hukumomin sojin Nijar sun hana zirga-zirga a tsakaninsu a yanzu ta hanyar ci gaba da garkame iyakar kasashen.

People are also reading