Home Back

Bangaren Maza Ko Mata? Hukumar Gidan Yari Ta Fadi Sashen da Za Ta Ajiye Bobrisky

legit.ng 2024/5/16
  • Daga karshe, hukumar kula da gidajen yari a Najeriya, NCS ta bayyana sashen da za ta ajiye ɗan daudu, Bobrisky a gidan gyaran hali
  • Hukumar ta ce za ta bi shaidar da ta samu daga kotu inda fitaccen ɗan daudun ya tabbatar da cewa shi namiji ne a gaban kotun
  • Wannan na zuwa ne bayan Babbar Kotun Tarayya ta gurfanar da Bobrisky kan zargin cin zarafin naira da wulakanta ta

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya (NCS) ta bayyana sashen da za ta shiga dan daudu, Idris Bobrisky.

Hukumar ta ce ta dauki matakin ne bayan fitaccen ɗan daudun ya bayyanawa kotu cewa shi namiji ne.

Wata majiya daga hukumar ta NCS ta bayyana haka ga 'yan jaridu a ranar Juma'a 12 ga watan Afrilu, cewar Punch.

Majiyar ta ce:

"Tun da ya riga ya bayyana jinsinsa a kotu, dole za mu yi amfani da abin aka gabatar daga kotu."

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Bai kamata ya ji tsoron cin zarafi daga wasu maza ba saboda jami'anmu za su ba shi dukkan kariya da ya ke bukata."

Tun farko, an kama Idris Okuneye da aka fi sani da Bobrisky kan zargin cin mutuncin naira Wanda ya sabawa dokar kasa.

Bayan hukumar EFCC ta cafke shi a jihar Legas, Bobrisky ya nemi sassauci inda ya ce bai san hakan laifi ba ne a Najeriya.

Bayan gurfanar da shi a gaban kotu tare da umartansa ya fayyace jinsinsa, Bobrisky ya fadawa kotun cewa shi jinsin namiji ne.

Asali: Legit.ng

People are also reading