Home Back

Sakamako ya fara fitowa a zaben Afirka ta Kudu

dw.com 2024/7/2
Yadda ake tattara sakamako a Afirka ta Kudu
Yadda ake tattara sakamako a Afirka ta Kudu

An soma samun sakamakon farko na zaben da aka yi a kasar Afirka ta Kudu, zaben da takara ta yi zafi a cikinsa a ranar Laraba.

Rahotanni sun tabbatar da cewa an makara wajen kada kuri'u a jiyan, inda wasu rumfunan zabe suka kasance a bude har cikin dare.

Kuri'un jin ra'ayin jama'a dai na ci gaba da nuna yiwuwar jam'iyyar ANC mai mulki na iya rasa rinjayen da take rike da shi a karo na farko cikin shekaru 30.

Hakan dai na nufin lallai ne jam'iyyar ta shiga hadaka da jam'iyya ko ma wasu kananan jam'iyyu kafin ta iya mulkar kasar.

Koda yake alamu dai na ci gaba da nuna damar jam'iyyar ta samu kuri'u mafi rinjaye, abin da zai bai wa shugaba mai ci Cyril Ramaphosa damar dorewa kan mulki.

People are also reading