Home Back

RUƊANIN SARAUTAR KANO: ‘Har yau kotu ba ta damƙa mana takardar dakatar da soke masarautu ko naɗi ba’ – Gwamnantin Kano

premiumtimesng.com 2024/7/2
KANO: Gwamna Abba ya ce zai sa hannu kan hukuncin da kotu za ta yanke wa wanda ya cinna wa masallata wuta har 17 suka rasu

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa har zuwa ranar Asabar ba a damƙa mata takardar umarnin dakatar da rushe masarautu da naɗin Sarki Muhammadu Sanusi II ba.

Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano, Haruna Isah-Dederi ne ya bayyana haka, kamar yadda rahotanni suka wallafa.

Gidan Radiyon Dala FM da ke Kano ya ruwaito a ranar Asabar Dederi ya na cewa, “Da an damƙa wa Gwamnatin Jihar Kano takardar, to shi ne zai fara sani, domin shi ne za a damƙa ta a gare shi, a matsayin sa na Kwamishinan Shari’a, kuma Antoni Janar na Jihar Kano.”

Idan ba a manta ba, Gwamna Abba a lokacin damƙa wa Sarki Muhammadu Sanusi II takardar shaidar kama mulki, ya yi zargin cewa a cikin dare ranar Alhamis aka shigar da ƙara, kuma a lokacin Mai Shari’a wanda ya bada umarnin ya na Amurka.

Mataimakin Gwamnan Kano, Kwamared Aminu Abdulsalam ya ce a Kano Sarki Muhammadu Sanusi II shi ne Sarki, babu wani da ya isa daga waje ya zo ya canja.

People are also reading