Home Back

Kyandar biri ta bulla a Kwango

dw.com 2024/5/10
Kyandar biri ta bulla a Kwango
Kyandar biri ta bulla a Kwango

Hukumomi a Jamhuriyar Dimokradiyyar Kwango sun tabbatar da bullar cutar kyandar biri a kasar ciki har da babban birnin kasar, Brazzaville. Ministan kiwon lafiya na kasar, Gilbert Mokoki ya ce an samu rahotanni mutum 19 da suka kamu da cutar.

Mista Mokoki ya ja hankalin jama'ar kasar da su dauki matakan dakile yaduwar cutar ta hanyar kaucewa cudanya da wadanda suka kamu da ita da kuma wasu dabobbi da ma kaucewa ta'amulli da danyen naman dabobbin dawa.

Kwararru a fannin kiwon lafiya sun bayyana cewa alamomin cutar sun hada da zazzabi da guraje da kuma marurai. A shekarar 1970 ne dai aka faro gano cutar ta kyandar biri a jikin dan Adam a kusa da Jamhuriyar Dimokradiyar Kwango a cewar Hukumar lafiya ta duniya WHO.

People are also reading