Hajji: Mahajjata Sun Kunyata Mahukuntan Najeriya, Sun Yi Zanga Zanga a Saudiyya
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Saudi Arabia: Mahajjatan Najeriya da suka fito daga birnin tarayya Abuja sun gudanar da zaga zangar lumana Makkah.
Mahajjatan sun ce an samu matsala kan kuɗaɗen guzurinsu da aka ce za a ba su idan sun isa kasa mai tsarki.
BBC Hausa ta ruwaito cewa mahajjatan sun zargi wasu daga cikin ma'aikata da yin ba daidai ba da kudin guzurin nasu.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Wasu daga cikin mahajjatan sun bayyana cewa tun suna gida Najeriya aka musu alkawarin kudin guzuri dala 500.
Amma sai ga shi an ba su dala 400, an zaftare musu dala 100, hakan kuma ya fusata su har suka tayar da zanga-zangar.
Wani mahajjaci ya tabbatar da cewa a lokacin da aka ba su dala 200 a Najeriya, an ce masu sai sun je kasa mai tsarki za a kara musu dala 300.
Hukumomin sun ce masu hakan ya faru ne saboda ƙarancin dalar Amurka a lokacin da suke ƙoƙarin tashi zuwa kasa mai tsarki.
Mahajjacin ya cigaba da cewa a lokacin da suka isa kasa mai tsarki sai aka ba su dala 200 maimakon dala 300 da aka yi masu alkawari.
Su kuma sai suka ga ba su da mafita sai dai su gudanar da zanga zanga domin nuna bacin rai da neman hakkinsu.
A wani rahoton, kun ji cewa hukumar alhazai ta kasa ta shawarci maniyyatan Najeriya masu bukatar kulawar lafiya da su ziyarci asibitocin gwamnatin Saudiyya.
NAHCON ta ce tana jiran amincewar Saudiya domin kafa asibitocinta a Makkah, yayin da ta samu izinin yin hakan a garin Madinah.
Asali: Legit.ng