Siyasar 2027: Tsohon 'Dan Majalisa Ya Hango Makomar Hadakar Atiku da Obi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Abuja- Tsohon dan majalisar wakilan Najeriya, Tajuddeen Yusuf ya ce abu ne mai matukar wahala Atiku Abubakar da Peter Obi su hade guri guda domin tunkarar zaben 2027.
Tsohon dan majalisar na wannan batu ne yayin da ake ganin tsofaffin 'yan takarar na bayyana cewa za su cure guri guda domin yin galaba a kan APC a kakar zabe mai zuwa.
Channels Television ta wallafa cewa tsohon dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar ya ce bai ga dalilin rashin hada kai da takwaransa na LP, Peter Obi ba.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Tsohon dan majalisar wakilai, Tajuddeen Yusuf ya ce kalaman Atiku Abubakar na nuni da cewa akwai matsala a kokarin hadewa da Peter Obi.
Atiku Abubakar kwanaki kadan bayan tattaunawarsu da Obi ya ce zai ci gaba da tsayawa takara matukar yana numfashi.
Vanguard News ta ruwaito wakilan Peter Obi na cewa ubangidansu ba shi da niyyar hadakar da ke neman kwace karfin ikon mulki kawai.
A cewar Tajuddeen Yusuf, duk da Peter Obi ya yiwa Atiku Abubakar mataimaki a zaben 2019, hakan zai yi matukar wahala a nan gaba.
A baya mun baku labarin cewa dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter Obi ya ce da gaske suke shirin doke APC a kakar zabe mai zuwa.
A karin bayani da ya yi kan hadakarsu da Atiku Abubakar, Obi ya ce matuƙar da gaske aka kuma aka samu fahimtar juna, zai bayar da hadin kai dari bisa dari.
Asali: Legit.ng