Home Back

An Kama Shugaban ’Yan Bindigar da Ake Zargin Sun Farmaki Jirgin Kasan Abuja-Kaduna

legit.ng 2024/6/14

Kaduna - Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce jami’anta sun kama wani Ibrahim Abdullahi (Mandi), wanda ake kyautata zaton shi ne ya kitsa harin jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna a watan Maris din 2022.

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Jaridar The Punch ta ruwaito kakakin rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, ne ya bayyana hakan a yayin ganawa da manema labarai a jihar Kaduna.

Ya bayyana cewa an kwato bindiga kirar AK-47 guda 48 yayin da ake tsare da shi bayan ci gaba da binciken da ake yi.

A cewar rahoton SaharaReporters, 'yan Adejobi ya jaddada yunkurin rundunar na gano wanda ya dauki nauyin Mandi da kuma wanda ya kawo makaman.

Karashen labarin na zuwa...

Asali: Legit.ng

People are also reading