An Kama Shugaban ’Yan Bindigar da Ake Zargin Sun Farmaki Jirgin Kasan Abuja-Kaduna
Kaduna - Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce jami’anta sun kama wani Ibrahim Abdullahi (Mandi), wanda ake kyautata zaton shi ne ya kitsa harin jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna a watan Maris din 2022.
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Jaridar The Punch ta ruwaito kakakin rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, ne ya bayyana hakan a yayin ganawa da manema labarai a jihar Kaduna.
Ya bayyana cewa an kwato bindiga kirar AK-47 guda 48 yayin da ake tsare da shi bayan ci gaba da binciken da ake yi.
A cewar rahoton SaharaReporters, 'yan Adejobi ya jaddada yunkurin rundunar na gano wanda ya dauki nauyin Mandi da kuma wanda ya kawo makaman.
Karashen labarin na zuwa...
Asali: Legit.ng