Home Back

Yarima bin Salman zai halarci taron G7

dw.com 2024/7/2
Yarima Mohammed bin Salman na Saudiyya
Yarima Mohammed bin Salman na Saudiyya

Yarima mai jiran gado na Saudiya, Mohammed Bil Salman zai bi sahun wasu shugabannin kasashe 12, da za su halarci taron koli na kasashe masu karfin arzikin masana'antu na G7 da kasar Italiya ke karbar bakunci. Gayyatar wasu shugabannin da ba kasafai ake ganin hakan ba, na daga cikin yunkurin Italiyar na kara fadada taron na G7, na manyan kasashen masu karfin tatattalin arziki a duniya.

Karin bayani: Kammala taron koli na kasashen G7

Ana kuma sa ran shugabannin kasashen Indiya da Afirka ta Kudu da Brazil da Argentina da Turkiyya da Algeria da Kenya da kuma Mauritania su halarci taron, na ranakun 13 zuwa 15 ga watan Yunin 2024. Wannan dai shi ne karon farko, da a ka  gayyaci wani shugaba daga kasar Saudiyya, da ake mata kallon mai take hakkin bil Adama zuwa taron na G7.

People are also reading